fidelitybank

‘Yan siyasa nna da hannu a kashe-kashen Imo – Uzodinma

Date:

Gwamna Hope Uzodinma na jihar Imo ya dora alhakin kashe-kashen da aka yi a jihar kan wasu ‘yan siyasa.

Uzodinma ya ce ’yan siyasa da ke adawa da jam’iyyar, APC ne ke haddasa kashe-kashe da rashin tsaro a jihar.

Ya yi wannan jawabi ne a cocin Cathedral of Transfiguration of Our Lord, CATOL, dake Owerri, babban birnin jihar jiya.

Gwamnan ya kuma ce, wadanda ke zargin shugaban kasa Muhammadu Buhari da rashin tsaro ne ke haddasa irin wadannan ayyuka.

Uzodinma ya yi nuni da cewa ‘ya’yan jam’iyyar PDP, ba su samu asarar rai ba, sabanin APC.

“Ina rokon Allah ya taba zukatan wadannan mutanen da ke daukar nauyin kashe wadanda ba su ji ba ba su gani ba, kona gidaje da lalata dukiyoyin al’umma da sunan siyasa.

“Tun da aka fara wannan kisan gilla a Orlu, Orsu da sauran al’umomin shiyyar, ba jam’iyyar PDP guda daya ta mutu ba, an kona gidajensu ko aka kai hari.

“Saboda haka, a bayyane yake a gare ni cewa wadannan kashe-kashen na hannun ‘yan siyasa ne da ke bin ‘yan APC,” in ji Uzodinma.

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...
X whatsapp