Gwamna Hope Uzodinma na jihar Imo ya dora alhakin kashe-kashen da aka yi a jihar kan wasu ‘yan siyasa.
Uzodinma ya ce ’yan siyasa da ke adawa da jam’iyyar, APC ne ke haddasa kashe-kashe da rashin tsaro a jihar.
Ya yi wannan jawabi ne a cocin Cathedral of Transfiguration of Our Lord, CATOL, dake Owerri, babban birnin jihar jiya.
Gwamnan ya kuma ce, wadanda ke zargin shugaban kasa Muhammadu Buhari da rashin tsaro ne ke haddasa irin wadannan ayyuka.
Uzodinma ya yi nuni da cewa ‘ya’yan jam’iyyar PDP, ba su samu asarar rai ba, sabanin APC.
“Ina rokon Allah ya taba zukatan wadannan mutanen da ke daukar nauyin kashe wadanda ba su ji ba ba su gani ba, kona gidaje da lalata dukiyoyin al’umma da sunan siyasa.
“Tun da aka fara wannan kisan gilla a Orlu, Orsu da sauran al’umomin shiyyar, ba jam’iyyar PDP guda daya ta mutu ba, an kona gidajensu ko aka kai hari.
“Saboda haka, a bayyane yake a gare ni cewa wadannan kashe-kashen na hannun ‘yan siyasa ne da ke bin ‘yan APC,” in ji Uzodinma.