fidelitybank

‘Yan siyasa na barazana ga zaben 2023 – Jega

Date:

Tsohon shugaban hukumar zabe, INEC, Farfesa Attahiru Jega, ya ce, ‘yan siyasa da ma masu zabe su ne babbar barazana ga nasarar zabukan da ke tafe na kasar, na ranar 25 ga watan nan na Fabrairu da kuma na 11 ga watan Maris.

Ya fadi hakan ne a yayin da yake gabatar da babban jawabi jiya Talata a Abuja, a wurin taron wayar da kan jama’a kan muhimmancin zaman tare da hakuri da juna da kuma yin zabe cikin kwanciyar hankali da ba tare da wata matsala ba, wanda cibiyar Da’awa da Tabbatar da Jin Dadin Jama’a ta babban masallacin tarayya da ke Abuja ta shirya.

Farfesan ya ce wadanda ke kiran kansu ‘yan siyasa, da suka hada da masu takara su ne rukunin masu ruwa da tsaki a harkar da kusan za a iya cewa ba a ga wani sauyi na kirki a kan yadda suke gudanar da al’amuransu da suka danganci zabe ba tun 1999.

Karanta Wannan: Zaben 2023: INEC ta fara zaben gwaji na BVAS

”Burinsu kawai shi ne su yi nasara ta ko wane hali, inda suke daukar zabe a matsayin wani abu na ko a mutu ko a yi rai. Kamar yadda suke yi tun 1999, suna ci gaba da yin haka, kuma za su iya yin hakan a 2023,” in ji shi.

Jega ya kara da cewa; ”Yadda ba a hukunta su kan abin da suke yi, haka kuma suke kara dilmiya cikin magudi da miyagun abubun da suke yi. Wanda wannan ka iya zama babban kalubale ga zabukan 2023.”

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta É—aure Matashin da ya shiga É—akin kwanan ÆŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp