fidelitybank

‘Yan Sandan Zamafara sun yi ajalin wani dan bindiga

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, ta tabbatar da kashe wani dan bindiga tare kuma da kwato makamai a kan hanyar Gusau bayan samun rahoton yunkurin kai hari da ‘yan bindigar suka yi.

A wata sanarwa da mai magana da yawun ‘yan sandan jihar, SP Mohammed Shehu ya fitar, ya ce a ranar 1 ga watan Janairu ne suka samu nasarar fatattakar ‘yan bindigar zuwa cikin daji bayan artabu na tsawon lokaci, inda suka kwato bindigar AK-47 da harsasai 104 da kuma wasu abubuwan yin asiri daga hannun ‘yan bindigar.

Har ila yau, sanarwar ta Æ™ara da cewa wata rundunarta ta musamman ta kama wasu mutum shida da ake zargi da aikata ta’addanci da garkuwa da mutane da kuma satar shanu, ciki har da wani mai bai wa ‘yan bindiga bayanai da ke Æ™ananan hukumomin Zurmi da Shinkafi na jihar.

Kakakin ‘yan sandan ya ce wadanda ake zargin na hannun ‘yan sanda, inda suke bayar da bayanai da za su kai ga kamo sauran masu laifi, inda ya ce bayan haka za a tura su zuwa kotu domin yi musu hukunci bayan kammala bincike.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haÉ—a gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon É—an majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

ÆŠanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

ÆŠanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon É—antakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...
X whatsapp