fidelitybank

‘Yan sandan sun kama mutanen da ake zargi da yi wa mace tsirara a titi

Date:

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce ta kama mutum shida da zargin yi wa wata mata tsirara tare da yin holenta a titi.

Lamarin ya faru ne a garin Aguleri da ke Jihar Anambra a kudancin ƙasar bayan mutanen sun zarge ta da hannu a mutuwar mijinta saboda lalata da take yi da wasu mazan, zargin da ta musanta.

Daga cikin waɗanda aka kama akwai wani mai maganin gargajiya da ya kula da mijin nata, wanda daga baya ya faɗa wa ‘yan uwansa cewa matar na da hannu wajen mutuwarsa.

‘Yan sanda sun kama mutanen bayan wani bidiyo ya karaɗe shafukan zumunta, inda ya nuna mutanen suna yawo da matar a titi tsirara. ‘Yan Najeriya da dama sun nuna ɓacin ransu da ganin bidiyon.

Mai magana da yawun ‘yan sandan Anambra ya faɗa wa BBC cewa suna gudanar da bincike kan mutanen da suka kama da zargin abin da suka kira laifin cin zarafi kafin a kai su kotu.

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp