Jami’an ‘yan sanda a Katsina sun dakile hare-haren ‘yan ta’adda a kauyukan Marina, Garin Zaki, Kadage, da ‘Yar-tsamiya da ke kananan hukumomin Safana, Batsari, Kurfi, da Musawa a jihar.
A ci gaba da dakile harin da ‘yan ta’addan suka kai, an kashe dan ta’adda daya tare da kubutar da wasu mata uku da aka yi garkuwa da su. An samu nasarar kwato bindigu kirar AK-47 guda uku da harsashi guda goma sha biyar (15) 7.62MM da kuma babura guda biyu (2) na ‘yan ta’addan.
Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Gambo Isah, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis.
“A ranar 26/04/2022, an samu kiran gaggawa cewa ‘yan ta’addar da yawansu dauke da bindigogi kirar AK-47, sun kai hari kauyen Marina, karamar hukumar Safana. Sakamakon haka, DPO Safana ya jagoranci tawagar ‘yan sanda da na ‘yan banga hadin gwiwa zuwa yankin inda suka yi artabu da ‘yan ta’addan a wani artabu da bindiga.