fidelitybank

‘Yan sandan Kadun sun kubutar da mutumin da aka yi garkuwa da shi

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta kuɓutar da wani mutum da masu garkuwa da mutane suka kama a Abuja suka kuma nufi jihar da shi.

Cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ta ce ta kuɓutar da mutumin wanda aka yi garkuwa da shi a Abuja babban birnin ƙasar ranar Laraba da maraice.

Rundunar ta ce a ranar Alhamis 18 ga watan Janairu ta samu rahoton yin garkuwa da wani mutum a Abuja, inda aka yi zargin masu garkuwar sun tafi da mutumin da suka sacen zuwa jihar Kaduna.

Daga nan ne rundunar ta ce jami’anta suka riƙa sanya idanu kan zirga-zirgar motocin da ke shiga jihar daga birnin na Abuja.

Sanarwar ta kuma ce da misalin ƙarfe 1:00 na rana ne jami’nta suka tare wata mota ƙirar Toyota mai launin ruwan toka, wadda ke ɗauke da mutum huɗu ciki har da direban, inda suka yi zargin masu garkuwar ne a ciki.

Yayin da mutanen suka ga ‘yan sanda sun tare su sai suka yi yunƙurin tserewa, inda ɗaya daga cikinsu ya buɗe wuta wa ‘yan sandan, waɗanda su ma nan take suka mayar da martani.

Inda ɓangorin biyu suka buɗe wa juna wuta, lamarin da ya sa ‘yan sandan suka ƙubutar da wanda aka yi garkuwar da shi mai suna Segun Akinyemi da ke zaune a unguwar Area 3, Garki Abuja, tare da kama ɗaya daga cikin masu garkuwar mai suna Chinaza Philip da ke unguwar Life Camp a Abuja, inda sauran mutum uku suka tsere, waɗanda rundunar ta ce tana ci gaba da farautarsu.

Rundunar ta kuma ce ta ƙwato motar wadda ta mutumin da aka yi garkuwar da shi ne, da kuma ƙananan bindigogi nau’ikan Pistol da harsasai masu yawa daga wajen masu garkuwar.

Binciken farko ya nuna cewa maharan sun kama mutumin ne ranar Laraba 17 ga watan Janairu lokacin da ya fita daga gidansa da yamma.

Maharan na kan hanyarsu ta kai mutumin zuwa Kano a lokacin da ‘yan sandan suka kama shi.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp