Rundunar ‘yan sandan jihar Edo, a ranar Laraba, ta ce, jami’anta sun kashe wasu mutane shida da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a yayin wani artabu da suka yi da su.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Kontongs Bello, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, ya ce, masu garkuwa da mutane sun tare wata motar bas mai kujeru 18 da ta taso daga Legas zuwa Gabashin kasar nan ta hanyar Legas zuwa Benin.
A cewarsa, masu garkuwa da mutanen sun yi awon gaba da wadanda abin ya shafa cikin dajin ne a lokacin da suka gamu da ‘yan sanda suka yi artabu da su, inda ya ce, masu garkuwar sun mutu ne sakamakon raunukan da suka samu a yayin fafatawar.
Ya ce, ana kyautata zaton wadanda suka mutun na cikin gungun ‘yan ta’adda da ke addabar babbar hanyar Benin/Lagos da kewaye.
A cewarsa, an kubutar da fasinjojin ne ba tare da jin rauni ba, yayin da ake ci gaba da tonon sililin dajin domin kame wasu ’yan kungiyar da suka gudu, ya kara da cewa an samu bindigar famfo guda daya a wurin.