fidelitybank

‘Yan sandan Edo sun kashe ‘yan ta’addar da suka addabi hanyar Benin zuwa Legas

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Edo, a ranar Laraba, ta ce, jami’anta sun kashe wasu mutane shida da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a yayin wani artabu da suka yi da su.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Kontongs Bello, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, ya ce, masu garkuwa da mutane sun tare wata motar bas mai kujeru 18 da ta taso daga Legas zuwa Gabashin kasar nan ta hanyar Legas zuwa Benin.

A cewarsa, masu garkuwa da mutanen sun yi awon gaba da wadanda abin ya shafa cikin dajin ne a lokacin da suka gamu da ‘yan sanda suka yi artabu da su, inda ya ce, masu garkuwar sun mutu ne sakamakon raunukan da suka samu a yayin fafatawar.

Ya ce, ana kyautata zaton wadanda suka mutun na cikin gungun ‘yan ta’adda da ke addabar babbar hanyar Benin/Lagos da kewaye.

A cewarsa, an kubutar da fasinjojin ne ba tare da jin rauni ba, yayin da ake ci gaba da tonon sililin dajin domin kame wasu ’yan kungiyar da suka gudu, ya kara da cewa an samu bindigar famfo guda daya a wurin.

ng news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...
X whatsapp