fidelitybank

‘Yan sandan Abuja sun kama dilan Wiwi mai shekaru 20

Date:

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayyar Abuja a ranar Asabar ta ce, ta kama wani matashi dan shekara 20 mai suna Abubakar ishiaku, dauke da buhu 20 na kayan maye da ake zargin tabar wiwi.

Kwamishinan ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, Babaji Sunday, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar, ya ce, wanda ake zargin ya kaucewa kamun da jami’an ‘yan sandan suka yi ne bayan ya gansu a wani bincike na sirri.

A cewarsa, wasu ‘yan sanda sun tsaya ne da bincike a ranar 12 ga Yuli, 2022.

Kwamishinan ya kara da cewa, wanda ake zargin dan asalin jihar Katsina ne, an sake kama shi ne a ranar 14 ga watan Yuli bayan gudanar da bincike mai zurfi.

Sanarwar ta ce, “Wanda ake zargin wanda ya yi kasa a gwiwa lokacin da ya ga ‘yan sandan suna bakin aiki a ranar da aka ce an sake kama shi ne a ranar 14 ga Yuli, 2022 bayan bincike mai zurfi yayin da aka gano buhu 20 na busasshen ganyen da ake zargin na Indiyawan Hemp ne,” in ji sanarwar.

Kwamishinan ‘yan sandan ya kara da cewa, za a mika wanda ake zargin ga hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, domin gurfanar da shi gaban kuliya.
Ya ce ‘yan sanda na hada kai da hukumar NDLEA wajen damke dilolin miyagun kwayoyi.

nigerian 
newspapers today the sun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp