Jami’an rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, sun samu nasarar fatattaki ‘yan bindiga da dama tare da ceto wasu mutane 16 da aka yi garkuwa da su a wasu dazuzzukan da ke kan iyaka da Abuja da jihar Kogi.
Dangane da bayanan sirri, a cewar wata majiya, ‘yan sandan sun far wa dazuzzukan ne a ranar Lahadi 1 ga watan Janairu, 2023, biyo bayan rahotannin sace-sacen mutane a kauyukan Anguwan Yango, Gulida, Chakumi, da Paikon Bassa a karamar hukumar Abaji.
Wata majiya ta ce ‘yan bindigar dauke da muggan makamai sun yi ta harbin kan mai uwa da wabi na tsawon sa’o’i, inda suka nuna jin dadinsu da yadda jami’an tsaron suka yi galaba a kansu tare da kubutar da wasu mutane 16 da aka yi garkuwa da su daga cikin matsugunin su, yayin da ‘yan fashin suka gudu.
Jami’ar hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, Josephine Adeh, ta bayyana cewa tuni wadanda aka ceto suka koma ga iyalansu.
“An kai wadanda aka ceto zuwa asibiti daga bisani kuma suka sake haduwa da iyalansu,” in ji ta.