fidelitybank

‘Yan Sandan Abuja sun fatattaki ‘yan bindiga

Date:

Jami’an rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, sun samu nasarar fatattaki ‘yan bindiga da dama tare da ceto wasu mutane 16 da aka yi garkuwa da su a wasu dazuzzukan da ke kan iyaka da Abuja da jihar Kogi.

Dangane da bayanan sirri, a cewar wata majiya, ‘yan sandan sun far wa dazuzzukan ne a ranar Lahadi 1 ga watan Janairu, 2023, biyo bayan rahotannin sace-sacen mutane a kauyukan Anguwan Yango, Gulida, Chakumi, da Paikon Bassa a karamar hukumar Abaji.

Wata majiya ta ce ‘yan bindigar dauke da muggan makamai sun yi ta harbin kan mai uwa da wabi na tsawon sa’o’i, inda suka nuna jin dadinsu da yadda jami’an tsaron suka yi galaba a kansu tare da kubutar da wasu mutane 16 da aka yi garkuwa da su daga cikin matsugunin su, yayin da ‘yan fashin suka gudu.

Jami’ar hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, Josephine Adeh, ta bayyana cewa tuni wadanda aka ceto suka koma ga iyalansu.

“An kai wadanda aka ceto zuwa asibiti daga bisani kuma suka sake haduwa da iyalansu,” in ji ta.

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp