Rundunar ‘yan sandan Jihar Zamfara sun kama 12 da ake zargi da laifuka daban-daban a fadin jihar da suka danganci ayyukan ‘yan bindiga da mu’amala da makamai da kuma bangar siyasa.
Rundunar ta kuma kwato wasu bindigogi da aka ƙera da bindigar AK-47 da harsasai 100 da adda da wasu abubuwan yin asiri daga wajen mutanen. An gurfanar da wadanda ake zargin a hedkwatar hukumar ‘yan sandan jihar da ke Gusau
Kakakin ‘yan sandan jihar, SP Mohammed Shehu, ya ce mutum biyar cikin wadanda ake zargin an kama su ne da laifin yin bangar siyasa da kuma ke da hannu a harbe-harben bindiga da janyo mutuwar wani mutum daya da jikkata wasu 11.
SP Shehu ya kuma ce wadanda ake zargin sun hada da Lawali Yakubu da Aminu Abubakar da Shuaibu Mohammed da Abdulmumini Bawa da kuma Sirajo Yahaya.