Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi, ta tabbatar da kashe wasu mutum huɗu da ‘yan bindiga suka yi a anguwar Gambari Sabon-Layi da ke karamar hukumar Tafawa Balewa na jihar.
Mai magana da yawun ‘yan sandan jihar, SP Ahmed Wakili, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN a ranar Lahadi a Bauchi.
Ya ce ‘yan bindigar sun farwa anguwar ne da tsakar daren ranar Asabar, inda suka yi garkuwa da mutum ɗaya.
Ya ce Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Aminu Alhassan, ya bayar da umarnin gudanar da bincike don kama waɗanda ke da laifi.