‘Yan sandan reshen Jihar Katsina, sun ceto mutum 21 da ‘yan fashi suka yi garkuwa da su.
Dakarun sun yi nasarar ceto mata 15 da yara shida ne a yankin Ƙaramar Hukumar Dutsinma ta jihar da ke arewacin Najeriya.
Da misalin ƙarfe 4:30 na yamma ne rundunar ta samu kiran gaggawa cewa ‘yan bindiga masu yawa a kan babura na harbe-harbe da bindigogi ƙirar AK-47 a ƙauyukan Buraji da Sabon Sara, a cewar sanarwar da SP Gambo Isa ya fitar ranar Juma’a.
Da samun rahoton ne kuma kwamandan yanki ACP Mohammed Makama ya jagoranci dakaru inda suka toshe hanyar da maharan ke bi a ƙauyen Gandun Sarki, suka far musu kuma suka yi nasarar ƙwato mutanen.
SP Gambo ya ce an kashe ‘yan bindigar da dama sannan wasu sun tsere da raunuka.