fidelitybank

‘Yan sanda sun yi artabu da ‘yan ta’addan Kaduna

Date:

Jami’an rundunar ‘yan sanda reshen jihar Kaduna, sun yi artabu da ‘yan ta’adda, inda suka kashe mutane biyu a cikin lamarin.

Rundunar ‘yan sandan jihar ta tabbatar da hakan a wata sanarwa da kakakinta DSP Muhammed Jalige ya rabawa manema labarai a ranar Lahadi.

Jalige ya ce, an sanar da hukumar ne game da wani harin sace-sacen da aka yi a kauyen Timburku da ke unguwar Galadimawa a karamar hukumar Giwa inda suka yi gaggawar ceto wadanda lamarin ya shafa.

Sanarwar ta ce: “Bayan samun rahoton ta hannun DPO Kidandan a ranar Asabar, 23 ga Yuli, 2022 da misalin karfe 0800 na safe cewa wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wasu manoma da ba a tantance adadinsu ba da ke aiki a gonakinsu a kauyen Timburku, gundumar Galadimawa ta karamar hukumar Giwa, kwamishinan Rundunar ‘yan sanda, CP Yekini Ayoku, ya umurci rundunar ‘yan sanda da ke kusa da Operation Restore Peace (wanda aka yiwa lakabi da Operation Puff Adder II) zuwa yankin.”

Jalige ya ci gaba da bayanin cewa, kwararrun ‘yan sandan da suka tattaru zuwa wurin sun yi galaba akan ‘yan ta’addan duk da turjiya.

Biyu daga cikin ‘yan bindigar a cewar rundunar an kashe su ne yayin da jami’an tsaron suka kuma kwato bindiga kirar AK47 guda daya dauke da alburusai guda biyu, babur daya da kuma adduna yayin da aka ceto manoman da aka yi garkuwa da su.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp