Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa, ta tabbatar da kashe wani mutum mai suna Halliru Lafka a wani rikici da ya barke tsakanin ‘yan hamayya a wani gangamin yakin neman zaben jam’iyyar APC mai mulki a karamar hukumar Kazaure.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP. Emmanuel Ekot Effiom ya tabbatarwa manema labarai faruwar lamarin.
Ya ce ‘yan sanda suna farautar wanda ake zargi da kisan wanda aka ce ya bace zuwa makwabciyar jihar Kano bayan ya aikata laifin.
A cewar sa, “’yan sanda na kan gaba wajen ganin an kama wanda ake zargin ya gudu zuwa Kano.”
Ya ce rikicin ya faru ne a daren ranar Talata tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar APC guda yayin taron gangamin jam’iyyar.
DAILY POST ta tattaro cewa marigayin mazaunin garin Kazaure ne kuma babban mai goyon bayan dan takarar Sanata ne na jam’iyyar APC mai wakiltar Jigawa ta arewa maso yamma, Babangida Husseini.
Lamarin ya haifar da zanga-zangar da wasu mazauna garin suka yi inda suka kunna wuta tare da lalata allunan talla.
CP Ekot ya ce ‘yan sanda na kan gaba a lamarin kuma sun maido da zaman lafiya a yankin.