fidelitybank

‘Yan sanda sun tabbatar da kashe magoyin bayan APC a Jigawa

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa, ta tabbatar da kashe wani mutum mai suna Halliru Lafka a wani rikici da ya barke tsakanin ‘yan hamayya a wani gangamin yakin neman zaben jam’iyyar APC mai mulki a karamar hukumar Kazaure.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP. Emmanuel Ekot Effiom ya tabbatarwa manema labarai faruwar lamarin.

Ya ce ‘yan sanda suna farautar wanda ake zargi da kisan wanda aka ce ya bace zuwa makwabciyar jihar Kano bayan ya aikata laifin.

A cewar sa, “’yan sanda na kan gaba wajen ganin an kama wanda ake zargin ya gudu zuwa Kano.”

Ya ce rikicin ya faru ne a daren ranar Talata tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar APC guda yayin taron gangamin jam’iyyar.

DAILY POST ta tattaro cewa marigayin mazaunin garin Kazaure ne kuma babban mai goyon bayan dan takarar Sanata ne na jam’iyyar APC mai wakiltar Jigawa ta arewa maso yamma, Babangida Husseini.

Lamarin ya haifar da zanga-zangar da wasu mazauna garin suka yi inda suka kunna wuta tare da lalata allunan talla.

CP Ekot ya ce ‘yan sanda na kan gaba a lamarin kuma sun maido da zaman lafiya a yankin.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp