fidelitybank

‘Yan sanda sun tabbatar da kashe magoyin bayan APC a Jigawa

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa, ta tabbatar da kashe wani mutum mai suna Halliru Lafka a wani rikici da ya barke tsakanin ‘yan hamayya a wani gangamin yakin neman zaben jam’iyyar APC mai mulki a karamar hukumar Kazaure.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP. Emmanuel Ekot Effiom ya tabbatarwa manema labarai faruwar lamarin.

Ya ce ‘yan sanda suna farautar wanda ake zargi da kisan wanda aka ce ya bace zuwa makwabciyar jihar Kano bayan ya aikata laifin.

A cewar sa, “’yan sanda na kan gaba wajen ganin an kama wanda ake zargin ya gudu zuwa Kano.”

Ya ce rikicin ya faru ne a daren ranar Talata tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar APC guda yayin taron gangamin jam’iyyar.

DAILY POST ta tattaro cewa marigayin mazaunin garin Kazaure ne kuma babban mai goyon bayan dan takarar Sanata ne na jam’iyyar APC mai wakiltar Jigawa ta arewa maso yamma, Babangida Husseini.

Lamarin ya haifar da zanga-zangar da wasu mazauna garin suka yi inda suka kunna wuta tare da lalata allunan talla.

CP Ekot ya ce ‘yan sanda na kan gaba a lamarin kuma sun maido da zaman lafiya a yankin.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp