fidelitybank

‘Yan sanda sun tabbatar da ceto Dalibai 20 da aka sace a Benue

Date:

Rundunar ƴansanda ta tabbatar da sakin ɗaliban nan 20 da ke karatun aikin likita, waɗanda aka sace a jihar Benue a ranar Juma’a ta makon da ya gabata.

A wata sanarwa da kakakin ƴansandan ƙasar, Muyiwa Adejobi, ya fitar ya ce a jiya Juma’a ne ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, ya ceto ɗaliban da aka riƙe su a dajin Ntunkon, da ke ƙaramar hukumar ADO ta jihar Benue, ba tare da an biya wani kuɗi ba.

Tashar talabijin ta Channels, ta ce wata majiya da ta tabbatar da ingancinta, ta tabbatar mata cewa an yi amfani da wasu jiragen yaƙi masu sauƙar ungulu guda uku a aikin ceto ɗaliban, inda ta ce an kama wasu daga cikin masu garkuwar wasu kuma an kashe su.

A ranar Alhamis ta makon da ya gabata ne aka sace ɗaliban na jami’ar Maiduguri da jami’ar Jos tare da likitocin da suke tare da su a kan hanyarsu ta zuwa wani taro.

Ƴan kwanaki kaɗan bayan sace su, ƴan bindigar sun tuntuɓi iyalan ɗaliban suna son a ba su kuɗin fansa naira miliyan 50, kafin su sake su.

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp