Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta samu nasarar kwato bindigogi kirar AK-47 guda biyu kowanne dauke da alburusai 30.
An kwato makaman ne daga hannun masu laifi da suka tsere daga hannun ‘yan sanda.
Kakakin rundunar ‘yan sandan Kaduna, DSP Muhammad Jalige, ya bayyana cewa “a ranar 18 ga Yuli, 2023, da misalin karfe 2205, jami’an rundunar ‘yan sandan Kaduna a lokacin da suke sintiri na yau da kullun a kan titin Hukunyi-Danja, iyaka tsakanin jihohin Kaduna da Katsina, sun hango wasu mutane biyu suna hawan babur cikin wani yanayi mai cike da shakku.
“Halin da ya sa tawagar ‘yan sintiri ta yi musu zagon-kasa, kuma da suka ga akwai hadari, nan take suka garzaya dajin da ke kusa don gudun kada a kama su.”
Ya kuma kara da cewa, a sakamakon haka, jakunan barayin sun fado daga kan babur din, inda ya jaddada cewa, a lokacin da aka binciko kayan, an kwato bindigogin AK-47 guda biyu dauke da harsashi guda 30 kowannensu.