Rundunar ‘yan sanda ta kasa ta sake cafke wani dan ta’addan Boko Haram, Hassan Hassan, wanda a kwanakin baya ya tsere daga gidan yarin Kuje.
Jaridar THEWILL ta ruwaito cewa, wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne a ranar Talata, sun kai hari a cibiyar gyara hali ta Kuje tare da kubutar da fursunoni sama da 800 da suka hada da ‘yan kungiyar Boko Haram da Islamic State West African Province (ISWAP).
A ranar Juma’a ne gwamnatin tarayya ta bayyana 69 daga cikin fursunonin, wadanda ake nema ruwa a jallo da sunayensu da wasu bayanai da aka buga.
Sanarwar da Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Nasarawa, DSP Ramhan Nansel ya fitar, ta ce an kama dan Boko Haram din ne da sanyin safiyar ranar Asabar, a karamar hukumar Keffi ta jihar.
Sanarwar ta ce, “Bayan harin da aka kai gidan kurkukun Kuje da kuma tserewar fursunonin a ranar 9 ga Yuli, 2022, da misalin karfe 0130 na safe, wani Hassan Hassan, ‘M’, wanda sunansa da hotonsa na daga cikin fursunonin da suka tsere tare da Boko Haram. /Al’amarin ta’addanci, jami’an ‘yan sanda masu ido da ido na rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa a Keffi sun sake kama su.
“Kwamishanan ‘yan sanda, CP Adesina Soyemi, ya bayar da umarnin mika wanda ake zargin zuwa wani wuri mafi aminci, yayin da ake ci gaba da neman sauran wadanda suka tsere tare da mika wadanda aka kama.