fidelitybank

‘Yan sanda sun kawar da ‘yan ta’adda 10 tare da kama wani rikake a Zamfara

Date:

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta sun yi nasarar kawar da ‘yan ta’adda 10 tare da kama wani dan fashi da makami a wani samame da suka kai a yankin Arewa maso Yamma.

Jami’in yada labarai na rundunar hadin guiwa ta Operation Hadarin Daji, Kaftin Yagata Ibrahim ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Gusau.

Ya ce sojojin sun kuma kama masu safarar makamai tare da kwato alburusai yayin samamen da suka kai jihohin Zamfara, Kebbi, Sokoto da Katsina.

Ibrahim ya ce sojojin sun samu gagarumar nasara wajen gudanar da ayyukan noman rani na hadin gwiwa a jihohin da abin ya shafa.

ā€œA wani samame na baya-bayan nan da suka kai a ranar 26 ga watan Janairu, sojojin sun yi nasarar fatattakar ā€˜yan ta’addan a kauyukan Pada, Matso-Matso da Yurlumu a karamar hukumar Batsari ta jihar Katsina.

ā€œA yayin farmakin an kashe ā€˜yan ta’adda bakwai yayin da wasu suka tsere da munanan raunukan harbin bindiga.

ā€œA wannan rana, sojojin OPHD a Zamfara da ke sintiri a yakin da suke yi sun kashe ā€˜yan ta’adda biyu a kauyukan Getso da Ubaka da ke karkashin karamar hukumar Maru.

“Sojojin sun kwato bindiga kirar AK-47 daya, mujalla daya da harsashi na musamman na 7.62mm da babura biyu,” in ji shi.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ę“ansandan jihar Kaduna, sun buʙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ʙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ā€˜Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ʙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ā€˜yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp