Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina sun yi nasarar halaka ‘yan ta’adda 2 masu tsayawa kan tituna suna yi wa matafiya fashi.
‘Yan sandan karkashin jagorancin DPO na Kankara, sun yi nasarar fatattakar miyagun da ke tsayawa a titin Zango zuwa Kankara a Katsina .
Ba a nan suka tsaya ba, sun samu nasarar ceto mutum 7 da suka hada da mata da jariransu kuma sun kwato dabbobi 142.
A ranar Laraba, tawagar ‘yan sanda sun yi nasarar dakile farmakin ‘yan ta’adda masu yawa, wadanda ke tare mutane su yi musu fashi a titin Zango zuwa Kankara cikin jihar Katsina, a cewar Vanguard.