Rundunar ‘yan sanda a jihar Ebonyi ta tabbatar da kashe biyu daga cikin ‘yan bindigar da suka kai hari a shelkwatar hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA) da ke jihar.
‘Yan bindigar sun kai hari ne a safiyar ranar Talata a ofishin hukumar NDLEA da ke Ntezi a karamar hukumar Ishielu a jihar.
Kakakin rundunar ‘yan sandan, DSP Loveth Odah, ta shaida wa kamfanin dillancin labarai na kasa NAN a Abakaliki cewa, ‘yan sandan sun kuma kwato makamai da alburusai da kuma layu a wurin su.
A cewar Guardian, ta kuma tabbatar da cewa, an kashe wani jami’in hukumar ta NDLEA da wani farar hula.
A cewarta, wasu daga cikin kayayyakin da aka kwato daga wurin da lamarin ya faru akwai bindigu guda biyu (AK-49 da K2) da kuma harsashi guda 140 K2.
Sauran harsashi na GPMP guda 36, harsashin bindigar barreta guda 65, Toyota 4Runner Jeep, wasu laya da sauran abubuwa masu tayar da hankali.