Hukumar tsaron farin kaya ta NSCDC, ta tabbatar da kai farmakin da jami’an ‘yan sandan suka kai wa rundunar ta Imo, wanda ya kai ga kashe wani jami’i tare da korar kwamandan jihar.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar, Olusola Odumosu, wanda ya tabbatar da harin a ranar Talata a Abuja, ya bayyana a matsayin abin takaici da tayar da hankali da jami’an ‘yan sanda suka yi ta kai wa jami’an hukumar hari tsawon shekaru.
Odumosu, ya ce hukumar ta Corps a halin yanzu tana tattaunawa da shugabannin ‘yan sanda, domin tabbatar da adalci da kuma kawo karshen cin zarafi da jami’an ‘yan sanda ke ci gaba da yi wa jami’an NSCDC.
Wasu ‘yan bindiga dauke da muggan makamai na squadron 18 ‘yan sandan kwantan da tarzoma da ke Owerri, sun mamaye shelkwatar hukumar NSCDC ta jihar Imo a ranar Litinin din da ta gabata, inda suka yi ta harbin iska, inda suka lakada wa jami’an NSCDC duka.
An yi zargin cewa ‘yan sandan sun yi garkuwa da jami’in ne bayan da suka mamaye harabar, inda suka lakada wa kwamandan, Mista Michael Ogar duka, wanda jin hayaniyar ya fito daga ofishinsa domin yin sulhu.