fidelitybank

‘Yan Sanda sun kama ‘yar bautar kasa ta bogi a sansanin NYSC

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta kama wata ƴar bautar ƙasa ta bogi mai suna Ogeh Bethel Chibuife bisa laifin shiga sansanin horaswa na Magaji Dan Yumusa da ke Keffi, babban birnin jihar ba bisa ka’ida ba.

Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ƴansandan Ramhan Nansel ya fitar, inda ya ce wadda ake zargin ta zo ne daga jami’ar jihar Ebonyi.

Nansel ya ce wadda ake zargin, wanda daliɓar ƙarin shekara ne daga Jami’ar Jihar Ebonyi, ta sulale ta shiga sansanin horaswa na NYSC wanda ake ɗaukar kwanaki 21 ana yi, da nufin samun horo a rukunin A, kashi na farko na 2024, inda daga bisani aka gano ta.

Ya ce wani jami’in NYSC ne ya kai rahoton lamarin ga ‘yan sanda a ranar Lahadi, kuma jami’an rundunar ne suka kama ta.

“Ta faɗa cewa a shekarar 2022 ya kamata ta kammala karatunta, ammasai ta faɗi wasu kwasa-kwasa, kuma a ƙoƙarinta na ɓoye karyar da ta yi wa iyayenta, ta je kasuwa ta siyo rigar kayan bautar ƙasa. Bayan ta sulale ta shiga cikin sansanin don ɗaukar hotuna ta aika wa iyayenta kafin aka kama ta,” in ji shi.

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp