fidelitybank

‘Yan Sanda sun kama ‘Yan Shi’a 97 a Abuja bayan kashe jami’ai

Date:

Rundunar ‘yan sanda ta ce, ta kama wasu mutane 97 na haramtacciyar kungiyar Islamic Movement of Nigeria (IMN), wadda aka fi sani da Shi’a, domin gurfanar da su gaban kuliya, bayan wata arangama da suka yi a Abuja ranar Lahadi.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya ruwaito cewa rikicin ya yi sanadiyar mutuwar ‘yan sanda biyu, yayin da wasu uku suka samu munanan raunuka.

NAN ta kuma ruwaito cewa ‘yan Shi’ar sun kona motocin sintiri uku a yayin arangamar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Abuja, ya ce sahihin bayanan sirri sun taimaka wa jami’an ‘yan sanda wajen cafke wadanda ake zargin.

Ya ce za a aiwatar da umarnin Sufeto-Janar na ‘yan sanda (IG), Mista Kayode Egbetokun kan lamarin.

Adejobi ya ce, I-G ya sake jaddada aniyar rundunar na cafke sauran mutanen da ke da hannu a harin tare da gurfanar da su a gaban kuliya.
Kakakin ‘yan sandan ya ambato I-G na cewa zai yi tir da duk wani rikici da tashe-tashen hankula a kowane bangare na kasar, ya kuma yi alkawarin ci gaba da tabbatar da doka da oda a dukkan sassan kasar.

A cewarsa, kashe-kashen ba gaira ba dalili da aka yi wa jami’an ‘yan sanda a bakin aikinsu, abin ban haushi ne kuma ba za a amince da su ba, domin wadanda suka kashe wadannan ‘yan sandan sun kashe zaman lafiya.

“Yayin da ake gudanar da bincike, rundunar ‘yan sandan Najeriya ta kuduri aniyar gano cikakken harin da aka kai tare da hana afkuwar irin wannan tashin hankali ga jami’an ‘yan sanda nan gaba,” inji shi.

Adejobi ya ce sufeto-janar ya jajantawa iyalan jami’an ‘yan sandan da suka rasu, ya kuma yi fatan samun sauki ga wadanda ake jinya a halin yanzu.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp