Rundunar ‘yan sandan jihar Kano, ta ce, ta kama mutane 85 waɗanda ta ke zargin ‘yan bangar siyasa ne tare kuma da ƙwato muggan makamai.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar , SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ta ce suna ci gaba da binciken mutanen da suka kama.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, ya gode wa al’umma jihar bisa haɗin-kai da suke bai wa rundunar, inda ya roki goyon bayansu wajen ganin an gudanar da zaɓe mai gaskiya a Najeriya.
A jiya ne dai aka samu rikici lokacin da magoya bayan jam’iyyar NNPP suka je tarbar ɗan takarar shugaban ƙasar na jam’iyyar, Injiniya Rabi’u Musa kwankwaso a jihar Kano lamarin da ya janyo jikkatar mutane da dama tare da ƙona motoci.
Jam’iyyar NNPP na zargin ‘yan jam’iyyar APC da kai musu harin a yayin da ‘yan APCn kuma suka musanta.