fidelitybank

‘Yan sanda sun kama soja da zargin fashi da mamaki a Yobe

Date:

Dubun wani soja da ke aikata fashi da makami ta cika, bayan an kama shi tare da wasu mutum biyu da zargin yin fashi a garin Damaturu, Jihar Yobe.

’Yan Sanda sun cafke sojan da abokan fashin nasa ne bayan sun kutsa gidan wata mata a unguwar Sabon Pegi da tsakar dare dauke da bindiga kirar AK 47 da sauran muggan makamai suka yi mata fashi.

An kama sojan da abokan fashinsa ne bayan sun yi wa matar awon gaba da mota kirar Peugeot 307 da tsabar kudi N250,000 da kuma wayar hannu kirar Nokia.

Mai magana yawun rundunar a jihar Yobe, ASP Dungus Abdulkarim ya tabbatar da hakan ga manema labarai ya na mai cewa, “Bayan an kama su, sun shaida wa ’yan sanda masu bincike cewa suna so ne su sayar da motar su raban kudin; Za a gurfanar da su a gaban kotu bayan kammala bincike” .

Ya kara da cewa ’yan fashin sun yi wa matar da danta mai shekara 17 rauni bayan sun daure su da wata waya a jikin turken faifen dauraron dan Adam.

ASP Dungus ya bayyana cewa an kama biyu daga cikin ’yan fashin ne a garin Damaturu, na ukunsu kuma wanda motar take hannunsa an kama shi ne a garin Darazo na Jihar Bauchi.

Aminiya ta rawaito cewa, ’yan sanda sun yi nasarar kwace makaman ’yan fashin da kuma duk kayan da suka yi fashi a gidan da suka shiga.

A cewarsa, Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Yobe, Haruna Garba, ya shawarci mazauna jihar da su kasance masu lura a abin da faruwa a zagaye da su, tare da taimaka wa jami’an tsaro da muhimman bayanai domin magance miyagun laifuka.

today nation

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp