fidelitybank

‘Yan sanda sun kama soja da zargin fashi da mamaki a Yobe

Date:

Dubun wani soja da ke aikata fashi da makami ta cika, bayan an kama shi tare da wasu mutum biyu da zargin yin fashi a garin Damaturu, Jihar Yobe.

’Yan Sanda sun cafke sojan da abokan fashin nasa ne bayan sun kutsa gidan wata mata a unguwar Sabon Pegi da tsakar dare dauke da bindiga kirar AK 47 da sauran muggan makamai suka yi mata fashi.

An kama sojan da abokan fashinsa ne bayan sun yi wa matar awon gaba da mota kirar Peugeot 307 da tsabar kudi N250,000 da kuma wayar hannu kirar Nokia.

Mai magana yawun rundunar a jihar Yobe, ASP Dungus Abdulkarim ya tabbatar da hakan ga manema labarai ya na mai cewa, “Bayan an kama su, sun shaida wa ’yan sanda masu bincike cewa suna so ne su sayar da motar su raban kudin; Za a gurfanar da su a gaban kotu bayan kammala bincike” .

Ya kara da cewa ’yan fashin sun yi wa matar da danta mai shekara 17 rauni bayan sun daure su da wata waya a jikin turken faifen dauraron dan Adam.

ASP Dungus ya bayyana cewa an kama biyu daga cikin ’yan fashin ne a garin Damaturu, na ukunsu kuma wanda motar take hannunsa an kama shi ne a garin Darazo na Jihar Bauchi.

Aminiya ta rawaito cewa, ’yan sanda sun yi nasarar kwace makaman ’yan fashin da kuma duk kayan da suka yi fashi a gidan da suka shiga.

A cewarsa, Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Yobe, Haruna Garba, ya shawarci mazauna jihar da su kasance masu lura a abin da faruwa a zagaye da su, tare da taimaka wa jami’an tsaro da muhimman bayanai domin magance miyagun laifuka.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp