Dubun wani soja da ke aikata fashi da makami ta cika, bayan an kama shi tare da wasu mutum biyu da zargin yin fashi a garin Damaturu, Jihar Yobe.
’Yan Sanda sun cafke sojan da abokan fashin nasa ne bayan sun kutsa gidan wata mata a unguwar Sabon Pegi da tsakar dare dauke da bindiga kirar AK 47 da sauran muggan makamai suka yi mata fashi.
An kama sojan da abokan fashinsa ne bayan sun yi wa matar awon gaba da mota kirar Peugeot 307 da tsabar kudi N250,000 da kuma wayar hannu kirar Nokia.
Mai magana yawun rundunar a jihar Yobe, ASP Dungus Abdulkarim ya tabbatar da hakan ga manema labarai ya na mai cewa, “Bayan an kama su, sun shaida wa ’yan sanda masu bincike cewa suna so ne su sayar da motar su raban kudin; Za a gurfanar da su a gaban kotu bayan kammala bincike” .
Ya kara da cewa ’yan fashin sun yi wa matar da danta mai shekara 17 rauni bayan sun daure su da wata waya a jikin turken faifen dauraron dan Adam.
ASP Dungus ya bayyana cewa an kama biyu daga cikin ’yan fashin ne a garin Damaturu, na ukunsu kuma wanda motar take hannunsa an kama shi ne a garin Darazo na Jihar Bauchi.
Aminiya ta rawaito cewa, ’yan sanda sun yi nasarar kwace makaman ’yan fashin da kuma duk kayan da suka yi fashi a gidan da suka shiga.
A cewarsa, Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Yobe, Haruna Garba, ya shawarci mazauna jihar da su kasance masu lura a abin da faruwa a zagaye da su, tare da taimaka wa jami’an tsaro da muhimman bayanai domin magance miyagun laifuka.