fidelitybank

‘Yan sanda sun kama mutumin da Dogara ya yi korafi a kansa na barazana

Date:

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi, Umar Sanda ya ce, rundunar ta kama wani mai rike da makamai mai ritaya a yayin da take fadada bincike kan ikirarin da tsohon kakakin majalisar wakilai, Yakubu Dogara ya yi na barazana ga rayuwarsa.

Sanda ya shaida wa manema labarai a ranar Lahadi a Bauchi cewa, an kama ma’aikacin mai ritayar ne bisa zargin bacewar bindigogi daga rumbun ajiyar makamai na rundunar.

Mista Sanda ya ce ya bayar da umarnin a binciki ma’ajiyar makamai na rundunar, ya kara da cewa baya ga bindigu biyu da aka kama, har yanzu ba a tantance bindigar ba.

“Mun fadada bincikenmu,” in ji shi, ya kara da cewa jami’in kula da kayan yaki da aka kama ya bar aikin shekaru biyu da suka gabata.

Dogara dai ya kai karar Sufeto Janar na ‘yan sandan kasar, inda ya zargi ‘yan sanda biyu da wani farar hula daya da suka hada baki domin su kawar da shi.

“Har yanzu ba mu tabbatar da ikirarin ba saboda mutum daya ya fito, amma mun tsananta bincike,” in ji kwamishinan ‘yan sandan.

Sanda ya kara da cewa “Za mu shaida wa duniya sakamakon binciken da zarar mun gama da shi, babu wani abu da za mu boye.”

legit nig. news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp