fidelitybank

‘Yan sanda sun kama mutanen da suke garkuwa har su 18 a Benue

Date:

Rundunar ‘yan sanda a jihar Benue, ta ce, jami’anta sun kama wasu mutum 18 da ake zargi da satar mutane tare da kwace makamai daga wajensu.

Mai magana da yawun rundunar, Catherine Anene Sewuese, cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin da maraice, ta ce mutanen da ake zargin sun yi kokarin tserewa jami’an ‘yan sanda a wani wajen binciken ababen hawa a kan hanyar karamar hukumar Utonkon inda aka kama su.

Ta ce an samu makamai a wajen mutanen ciki har da bindiga daya samfurin AK-47, da kananan bindigogi biyu da kuma alburusai da dama da aka nade a jarida.

Mai magana da yawun ‘yan sandan ta ce tuni aka kaddamar da bincike a kan mutanen wadanda yanzu haka ke hannun ‘yan sanda a tsare.

A bangare guda kuma, rundunar ‘yan sandan jihar Gombe ma ta ce ta kama wasu mutum biyu da take zargi da satar mutane da kuma mallakar makamai.

Cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ASP, Mahid Mu’azu, ya raba wa manema labarai, ya ce mutanen dukkansu daga karamar hukumar Dukku, an kama su ne a kan hanyarsu ta zuwa maboyar da suke taruwa a dajin Yankari da ke Bauchi.

Ya ce, an kama su ne a ranar 19 ga watan Augusta a kauyen Tudun Kwaya da ke karamar hukumar Biiliri tare da hadin gwiwar jami’an sintiri da mafarauta a yankin.

Ya ce koda aka tambayesu sun bayyana cewa suna daga cikin masu satar mutanen da ke addabar mutane a Pindiga.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp