fidelitybank

‘Yan sanda sun kama mutanen da su ka addabi Kano da kwacen waya

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama mutanen da a ke zargi da kwacen wayar hannu wanda su ka addabi al’ummar birnin Kano.

Mai magana da yawun rundunar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a ranar Lahadi.

Ya ce”Matakin ya biyo bayan umarnin da IGP ya bayar na kawar da duk wani nau’in laifuffuka da su ka hada da ‘yan daba (Daba) da shaye-shayen miyagun kwayoyi (Kwaya) da sauran munanan dabi’u na zamantakewa, musamman a wannan lokaci na bukukuwa”.

Kiyawa ya ce,”A yayin farmakin an kama mutane shida da a ke zargi, yayin da a ka kwato babura biyu masu kafa Uku da wayoyin hannu guda goma sha bakwai da a ka sace, wadanda a ke zargin sun kai hari tare da kwace wa fasinjojin su wayoyin hannu a babir mai kafa Uku.

 “A ranar 23/12/2021, ‘yan sanda sun samu rahoto daga mutane Takwas masu adireshi daban-daban cewa a rana guda a lokuta daban-daban, sun hau babur mai kafa 3, kuma mutanen da ke ciki sun hada baki su ka sace musu wayoyin hannu. Ba tare da bata lokaci ba rundunar mu ta kai dauki inda su ka yi nasarar kama Abubakar Abdullahi dan shekara 20 da ke Maiduguri jihar Borno da Abubakar Muhd ​​dan shekara 20 na Mubi jihar Adamawa da kuma Abdulkarem Abdullahi.”

“Haka kuma a ranar 24 ga Disamba, ‘yan sanda sun kama wani babur mai kafa 3 mai lamba FGG 216 QW da ta KAROTA DAL 19/1124 tare da mutum biyu, Sa’adu Jafar da Nafi’u Bala duk mazaunan unguwar Kurna Asabe Quarters da ke Kano”

 “A ranar 12/12/2021 da misalin karfe 1800, tawagar Operation Puff Adder suma yayin da su ke sintiri a Zango Quarters Kano sun kama Isma’il Jamilu dan shekara 18 da ke Dawaki Quarters Kano dauke da wayoyin hannu guda hudu (4)”.

Kiyawa ya ce za a gurfanar da wadanda a ke zargin a gaban kotu bayan sun kammala bincike a kan su.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Sama’ila Shu’aibu Dikko ya godewa gwamnati da al’ummar jihar Kano bisa addu’o’i da goyon baya da fahimtar juna da karfafa gwiwa da hadin kai da su ke bayarwa.

 

www.punch news.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...
X whatsapp