fidelitybank

‘Yan sanda sun kama matashi da kashe dan uwansa da wuka

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta kama wani matashi dan shekara 18 mai suna Abdurahman Sulaiman da laifin daba wa kaninsa wuka har lahira.

Ana zargin Sulaiman ya daba wa dan uwansa wuka ne a fafatawar da suka yi da juna, sakamakon zazzafar gardama a unguwar wasannin da ke cikin birnin Bauchi.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Umar Sanda wanda ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a ranar Asabar a Bauchi, ya ce gardamar ta biyo bayan wani gajeren wando ne da ake zargin na kanin wanda ake zargin ne.

Kwamishinan ya ce, a halin yanzu wadanda ake zargin suna hannunsu.

Ya ce wanda ake zargin ya kashe dan uwansa ne na jini a lokacin da babban ya bukace shi da ya cire wando da wanda ake zargin ya sanya, wanda yayan ya ce nasa ne.

Sanda ya ce, za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu bayan bincike, inda ya kara da cewa, ‘yan sanda ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen kamo masu aikata irin wadannan miyagun ayyuka.

CP ya kuma bukaci jama’a da su daina daukar doka a hannunsu.

Abdullahi Aminu, wanda ya shaida idonsa, ya ce, rigima ce aka caka wa kanin wuka a yayin fadan, sakamakon takaddama kan gajeren wando.

“Marigayin mai shekaru 20 da haihuwa, ana zargin ya bukaci kanensa Abdurahman da ya cire masa gajeren wando da yake sanye da ita, wanda ya ce na babban yayansa ne.

“Kanin ya ki cire shi, sai gardama ta barke, har ta kai ga fada.

“Kanin ya yi amfani da barasasshen gilashi ya daba wa kanin nasa wuka a ciki, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarsa,” in ji shi.

fg spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp