Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta kama wani matashi dan shekara 18 mai suna Abdurahman Sulaiman da laifin daba wa kaninsa wuka har lahira.
Ana zargin Sulaiman ya daba wa dan uwansa wuka ne a fafatawar da suka yi da juna, sakamakon zazzafar gardama a unguwar wasannin da ke cikin birnin Bauchi.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Umar Sanda wanda ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a ranar Asabar a Bauchi, ya ce gardamar ta biyo bayan wani gajeren wando ne da ake zargin na kanin wanda ake zargin ne.
Kwamishinan ya ce, a halin yanzu wadanda ake zargin suna hannunsu.
Ya ce wanda ake zargin ya kashe dan uwansa ne na jini a lokacin da babban ya bukace shi da ya cire wando da wanda ake zargin ya sanya, wanda yayan ya ce nasa ne.
Sanda ya ce, za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu bayan bincike, inda ya kara da cewa, ‘yan sanda ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen kamo masu aikata irin wadannan miyagun ayyuka.
CP ya kuma bukaci jama’a da su daina daukar doka a hannunsu.
Abdullahi Aminu, wanda ya shaida idonsa, ya ce, rigima ce aka caka wa kanin wuka a yayin fadan, sakamakon takaddama kan gajeren wando.
“Marigayin mai shekaru 20 da haihuwa, ana zargin ya bukaci kanensa Abdurahman da ya cire masa gajeren wando da yake sanye da ita, wanda ya ce na babban yayansa ne.
“Kanin ya ki cire shi, sai gardama ta barke, har ta kai ga fada.
“Kanin ya yi amfani da barasasshen gilashi ya daba wa kanin nasa wuka a ciki, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarsa,” in ji shi.