Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta kama wata mata mai shekaru 35, Hajiya Fatima Alhaji, da ake zargi ta na yi wa ‘yan bindigan da ke adabar jihar da kewaye asiri.
Mai magana da yawun ‘yan sandan jihar, SP Gamba Isah ne ya shaida wa manema labarai a ranar Alhamis, cewa an kuma gano Fatima ‘yar leken asirin ya bindiga ce.
Ya ce, ‘yan sandan sun kama Fatima mazauniyar Dajin Daha a karamar hukumar Danmusa a ranar 13 ga watan Fabrairu, bayan samun bayyanan sirri.
“Ta na taimaka musu, kuma ta na kai wa ‘yan bindigan da ke adabar jihar da kewaye bayanai, sannan ta na samar musu layyu da asiri. A yayin bincike, an gano wasu layyu daga gidan wacce ake zargin da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ke amfani da su, domin kai hari. Wacce ake zargin ta amsa cewa ta na kai wa wani Sani Mohidinge, hatsabibin shugaban ‘yan bindiga da ake dade a na nema magunguna,” in ji shi.