Rundunar ‘yan sandan jihar Benuwe, ta ce ta harbe wasu ‘yan bindiga hudu a karamar hukumar Ukum da ke jihar a wani samame da ta kai ranar Asabar.
Kwamishinan ‘yan sandan, Wale Abass, ya bayyana wadanda aka kashen kamar haka, Solo Orafaga, John Tyoakoso, Jude aka ‘Headboy’ da kuma wani dan bindiga da ba a tantance ba, wanda ya ce duk sun addabi Ukum.
A cewarsa, makaman da aka kwato daga hannunsu sun hada da bindiga kirar Ak47 guda daya, bindigar G3, bindigar gida da kuma alburusai da layu.
Da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar ‘yan sandan jihar da ke Makurdi, Abass ya yi alkawarin kawar da miyagun laifuka a jihar, tare da goyon bayan Gwamna Samuel Ortom.