Rundunar ‘yan sandan jihar Legas, ta gargadi mutanen jihar da suke shirin haifar da rikici bayan zaben jihar.
Jami’in hulda da jama’a, SP Benjamin Hundeyin ne ya bayar da sanarwar a yammacin Lahadi.
“Samun intel yana nuna wasu mutane sun kammala shirye-shiryen haifar da rikici da barna,” Hundeyin ya wallafa a shafinsa na twitter.
Karanta Wannan: Tinubu ya kaɗa kuri’arsa a jihar Legas
Kakakin ya yi gargadin cewa za a “murkushe irin wannan yunkurin”.
“Ba a rushe tsarin tsaro na zabenmu ba. Ba za a yarda da rashin zaman lafiya ba!,” ya jaddada.
An yi tashe-tashen hankula a sassa daban-daban na Legas yayin zaben na ranar Asabar yayin da ‘yan daba suka tarwatsa zabe, tare da lalata kayayyakin zabe.