Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta gargadi jam’iyyun siyasa da magoya bayansu, kan duk wani tashin hankali gabanin hukuncin kotun daukaka kara kan zaben gwamna a jihar.
Mukaddashin kwamishinan ‘yan sandan jihar, DCP Shettima Muhammad ya yi wannan gargadin yayin ganawa da manema labarai ranar Litinin a garin Lafiya.
Ya ce rundunar ‘yan sanda tare da hadin gwiwar sauran jami’an tsaro sun kara tsaurara matakan tsaro a fadin jihar domin dakile duk wata karya doka da oda kafin yanke hukunci da kuma bayan yanke hukunci.
“An tura jami’an tsaro isassu zuwa wurare masu mahimmanci a cikin Jihar domin wanzar da zaman lafiya.
“Don haka ina kira ga shugabannin jam’iyyun siyasa da su yi galaba a kan magoya bayansu da su nisanci kalaman da ba a tsare su ba da za su iya haifar da dambarwar siyasa ko kuma a yi wani gagarumin aiki da ake iya gani a matsayin shiri na tarzoma.
“Haka kuma su yi bikin tsaka-tsaki ba tare da keta haƙƙin jama’a ba.
“Duk wanda ko kungiyar da ke kokarin kawo cikas ga zaman lafiya da haifar da tabarbarewar doka da oda, za ta fuskanci fushin doka,” in ji shi.
A makon jiya ne kotun daukaka kara da ke Abuja ta dage shari’a kan karar da gwamnan jihar Abdullahi Sule na jam’iyyar APC ya shigar na neman a yi watsi da hukuncin kotun da tun farko ta soke zabensa.