fidelitybank

‘Yan Sanda sun fara kokarin ceto dan kasar Turkiyya a Abuja

Date:

Bayan da wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba suka yi awon gaba da wasu mutane biyu, cikinsu har da wani dan kasar Turkiyya, Erdogan Guler, mai shekaru 52, rundunar ‘yan sandan da ke yaki da masu garkuwa da mutane a babban birnin tarayya Abuja, ta fara gudanar da bincike wajen ceto su.

Wani babban jami’in ‘yan sanda ya shaidawa Vanguard cewa an tura jami’ansu zuwa Kubwa domin yin aiki tare da ‘yan sanda a karkashin rundunar Yansandan yankin.

Majiyoyi sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun bi sawun dan kasar Turkiyya da kuma wani mutum daya da ke tare da dan kasar Turkiyya zuwa wani katafaren gida da ke Kubwa, kusa da babbar hanyar Express inda suka yi awon gaba da su da bindiga da misalin karfe 7 na dare.

Daga baya an kai rahoto ga ‘yan sanda da ke ofishin ‘yan sanda na Dibishin Byazhin Abuja.

Wata majiya ta ce wasu ‘yan bindiga uku da ba a san ko su waye ba a cikin wata mota kirar Toyota Prado SUV, sun yi garkuwa da dan kasar Turkiyya da kuma wanda ke tare da shi a harabar sa (Guler) da ke Leaner Estate, Brickcity, Kubwa.”

Babban jami’in ya yi nuni da cewa, ba wai kawai kokarin kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su ba ne, har ma don bankado wadanda ke da hannu a wannan aika-aika da kuma kama su.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp