Kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi, CP Umar Mamman Sanda, ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan rikicin da ya barke a karamar hukumar Warji a jihar Bauchi, sakamakon ɓatanci ga addinin Islama da ake zargin wata mata ta yi a yankin Katangan.
Rundunar ƴan sandan jigar ta ce an samu jikkatar mutane da dama kuma an ƙona gidaje shida da shaguna bakwai sakamakon wani saƙon ɓatanci ga addinin Musulunci na wata mata mai suna Rhoda Jatau mai shekara 40 ma’aikatar lafiya a ƙaramar hukumar da aka wallafa a kafofin sada zumunta.
Wannan na zuwa bayan kisan wata ɗaliba Kirista a Sokoto da aka zarga ta zagi Annabi SAW a WhatsaApp
Rundunar ƴan sandan Bauchi ta ce jami’anta sun ƙoƙarin shawo kan rikicin kuma ƙura ta lafa yayin da suke ci gaba da aikin wanzar da zaman lafiya.