Jami’an ‘yan sanda da ke aiki da shiyya ta Magumeri a jihar Borno, sun dakile harin Boko Haram/ISWAP da sanyin safiyar Lahadi.
An tattaro cewa wasu da dama daga cikin ‘yan ta’adda dauke da makamai, wadanda ake zargin ‘yan kungiyar Islamic State of West African Province, (ISWAP) ne, sun afkawa rundunar ‘yan sanda reshen garin a cikin ayarin motocin bindigu da babura da misalin karfe 00:35. am.
Majiyar tsaron ta kuma shaidawa Zagazola Makama, kwararre a fannin yaki da ‘yan tada kayar baya, kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a yankin tafkin Chadi, cewa harin ya haifar da kazamin fada tsakanin jami’an ‘yan sanda da ‘yan ta’addan wanda ya kai har karfe 1:30 na safe.
Majiyar ta ce. jami’in sashen da mutanensa sun yi turjiya sosai tare da dakile shirin ‘yan ta’addan na mamaye su.
An ce wani Insifeto mai suna Bitrus Umaru ya samu rauni a harbin bindiga, an kuma kwace motar sintiri daya kirar Hilux, yayin da wata motar ‘yan ta’addar da ta kai hari ta kona wata motar ‘yan sanda ta daya daga cikin ‘yan sanda.