Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, ta sanar da dakile kai wasu hare-hare kan al’ummoin a kananan hukumomin Zurmi da Shinkafi na jihar.
Mai magana da yawun ‘yan sandan jihar, Mohammed Shehu, shi ya bayyana hakan yau Asabar yayin gabatar da wasu da ke da alaka da ‘yan bindiga da suka kama a Gusau, babban birnin jihar.
A cewar wata sanarwa da ‘yan sandan suka fitar, sun bayyana kama mutum uku wadanda ke bai wa ‘yan bindiga bayanan ayyukan jamia’an tsaro da kuma hada kai da su wajen sanya haraji kan wasu al’ummomi.
Sanarwar ta ci gaba da cewa , ‘yan sandan sun kuma kama wasu mutum shida da suka kware wajen samar wa ‘yan bindigan kwayoyi da suka haÉ—a da tabar wiwi da sauransu.
Ana ci gaba da bincike, inda bayan ne za a tura mutanen zuwa kotu domin hukunta su.