fidelitybank

‘Yan sanda sun cafke Murja ‘yar Tik Tok a Kano

Date:

Rundunar ‘yan sanda a jihar Kano, ta cafke fitacciyar jarumar wasan barkwanci ta TikTok, Murja Ibrahim Kunya, bisa zargin lalata da tarbiyyar al’umma.

Rundunar ‘yan sandan, kamar yadda Daily Nigerian ta ruwaito, ta cafke Murja ne a lokacin da take kokarin yiwa bakinta da suka zo daga nesa da kusa, domin bikin zagayowar ranar haihuwarta jamboree.

A watan Satumbar shekarar da ta gabata ne wata kotun shari’ar Musulunci ta rubutawa kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano da ya kama tare da binciki Murja Ibrahim Kunya tare da wasu ‘yan Tik Tokers guda 9 da laifin gurbata tarbiyyar al’umma.

Wasikar ta kara da cewa, “Bayan korafin da Muhd Ali Hamza Esq, Abba Mahmud, Esq, Sunusi I. Umar Esq, Abba, A.T Bebeji Esq, B.I Usman Esq, Muhd Nasir Esq, L.T Dayi Esq, G.A Badawi & suka shigar. Badamasi Suleiman Gandu Esq, Alkalin Kotun Shari’a ta Babban Kotun Shari’a na Bichi Kano ya umurce ni da in rubuta tare da neman ku da ku gudanar da bincike a kan wadanda ake zargin a sama domin daukar matakin da ya dace”.

Sauran Tik Tokers guda 9 da aka hada a cikin wasikar sun hada da: Mr 442, Safara’u, Dan Maraya, Amude Booth, Kawu Dan Sarki, Ado Gwanja, Ummi Shakira, Samha Inuwa da Babiana.

Ku tuna cewa a shekarar da ta gabata wata babbar kotun majistare ta yanke wa wasu matasa biyu Mubarak Isa da Nazifi Bala hukuncin bulala 20, da kuma yi wa al’umma hidima na tsawon kwanaki 30 bayan ta same su da laifin bata sunan gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje da kuma kara zage-zage. tashin hankali a cikin al’umma ta hanyar Tik Tok.

www.punch news.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp