Rundunar ‘yan sanda ta cafke wasu matasa dauke da muggan makamai, da nufin kawo cikas a zaben karamar hukumar Kunchi da ke jihar Kano.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Muhammad Usaini Gumel, ya bayyana cewa ba a samu wani tashin hankali ba a sake zaben da ake yi a rumfunan zabe 60 a kananan hukumomi shida da mazabu uku, amma rahotanni sun nuna an kama daruruwan matasa dauke da makamai. sun nufi kananan hukumomin Kunchi/Tsanyawa domin tada rikici da haifar da fargaba.
A karamar hukumar Tsanyawa, an ga yadda wasu matasa suka yi awon gaba da akwatunan zabe a yayin atisayen.
A halin da ake ciki kuma, an fara zaben majalisar dokokin jihar Kano cikin kwanciyar hankali a karamar hukumar Kura, inda masu kada kuri’a suka kada kuri’unsu.
Wakilinmu ya lura da kasancewar jami’an tsaro a dukkan runfunan zabe da ake sake gudanar da zabukan.
Jami’ar zabe mai zaman kanta a unguwar Kurunsumau dake yankin Auzinawa, Halima Abdullahi ta tabbatar da cewa na’urar BVAS na aiki sosai.
Zabuka na ci gaba da gudana lami lafiya a kusan daukacin rumfunan zabe na Kura.
A karamar hukumar Garun Malam, an ga kayan zabe sun isa kan lokaci, kuma masu kada kuri’a sun fito da wuri domin kada kuri’unsu.
Rahotanni daga mazabar Rimin Gado da Tofa na nuni da cewa zaben na ci gaba da gudana ba tare da wani cikas ba.
Jami’an tsaro suka cika da yawa a dukkan runfunan zabe, inda jama’a suka fito domin gudanar da aikin da kundin tsarin mulkin kasar ya ba su.