Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara a ranar Asabar da daddare ta bayar da belin wakilin jaridar Leadership, Umaru Maradun.
‘Yan sandan sun sako Maradun da misalin karfe 10:00 na dare. ranar Asabar.
An kama shi ne da sanyin safiyar ranar Asabar daga gidansa da ke Maradun, karamar hukumar Maradun kuma aka tsare shi a sashin binciken manyan laifuka (CID) Gusau.
Rundunar ‘yan sandan dai ba ta bayyana wani dalilin kama shi ba.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Ayuba Elkanah, ya bayar da umarnin a sake shi ga shugabannin kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ) bisa belin sa.
Sai dai Elkanah ya bayar da umarnin a mayar da Maradun, domin tattaunawa da shi ranar Litinin da karfe 7:30 na safe.
Shugaban kungiyar ‘yan jaridu ta NUJ na jihar, Ibrahim Maizare, ya sanya hannu kan yarjejeniyar mayar da Maradun ofishin ‘yan sanda a ranar.
Maradun, wanda ya zanta da manema labarai a ranar Lahadi, ya dage cewa, bai san wani laifi da ya sa aka kama shi ba.
Ya ce, ‘yan sandan sun isa gidansa ne a ranar 23 ga watan Yuli da misalin karfe 10:00 na safe, inda ya ce an gayyace shi ne domin ya yi masa bayani kan karar da aka shigar da shi.
Mista Maradun ya ce nan take aka mayar da shi hedikwatar rundunar da ke Gusau aka tsare shi.