fidelitybank

‘Yan Sanda sun bankado haramtacciyar matatar mai a Ribas

Date:

Jami’an Sufeto Janar na ‘yan sanda, IGP Special Task Force akan Man Fetur da Bunkering (IGP-STFPIB) sun kona wata haramtacciyar matatar mai a jihar Ribas.

Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya fitar a ranar Juma’a, ta ce an gudanar da farmakin ne a ranar Alhamis yayin da jami’an IGP-STFPIB tare da hadin gwiwar jami’an rundunar ‘yan sandan jihar suka kai farmaki a yankin Trans Amadi da ke Port-Harcourt babban birnin jihar Rivers. .

Sanarwar ta ce aikin ya biyo bayan gano wani wurin ajiyar kaya da ake amfani da shi wajen mu’amala da sarrafa danyen mai da aka samu ba bisa ka’ida ba a yankin.

Olumuyiwa ya tabbatar da cewa an kama akalla mutane hudu da ake zargi da aikata laifin, yana mai jaddada cewa an gano kimanin lita 40,000 na albarkatun man fetur da aka ajiye a cikin farar tankunan ajiya 67.

Wadanda ake zargin sun hada da Emmanuel Nwachi, Adamu Bala, Nura Musa da Bashir Abubakar.

“Duk da haka rundunar ta lalata wurin tare da kwato kayan aiki da injinan da aka yi amfani da su wajen aikata wadannan laifuka.

“Sfeto-Janar na ‘yan sanda, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, PhD, NPM., ya sake jaddada kudirin rundunar na magance duk wani nau’i na laifuka, aikata laifuka da cin hanci da rashawa, har zuwa ga wadanda ke da hannu a cikin wannan zagon kasa na tattalin arziki. Rundunar ta ci gaba da yin kasa a gwiwa, kuma za ta ci gaba da gurfanar da wadanda suka aikata laifin,” in ji sanarwar.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp