fidelitybank

‘Yan sanda a Zamfara sun ceto mutane 24 da aka yi garkuwa da su

Date:

Rundunar ƴan sandan Jihar Zamfara ta ceto mutum 24 waɗanda ƴan bindiga suka yi garkuwa da su a yankin.

A wata sanarwa da mai magana da yawun ƴan sandan jihar, SP Mohammed Shehu ya fitar, ya ce, tun da farko sun samu labarin harin da ƴan bindigan suka kai kan hanyar Gurgurawa a Ƙaramar Hukumar Bungudu ta Jihar Zamfara inda ƴan bindigar suka kwashi jama’a da dama.

Daga nan ne jam’ian ƴan sanda da ƴan bijilanti suka bazama cikin daji nemo waɗanda aka sace.

A cewar SP Mohammed, ko da ƴan bindigan suka hangi jami’an tsaro, sai suka soma harbi kan mai uwa da wabi wanda hakan ya ja aka ci gaba da musayar wuta tsakanin jami’an tsaron da ƴan bindigar.

Ya bayyana cewa, bayan wutar da ƴan bindigar suka sha, sai suka gudu suka bar waɗanda suka yi garkuwa da su.

Mutum 14 waɗanda akasarinsu mata ne aka ceto a wurin da lamarin ya faru, sauran mutum goma kuma a yayin da suke gudu neman ɗauki suka samu suka koma ƙauye ba tare da wani rauni ba.

Haka kuma rundunar ta ce, ta ƙwato babura bakwai waɗanda ƴan bindigan ke amfani da su yayin samamen da suka kai.

vangurd 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp