‘Yan sanda a Jamus sun kama wani ɗan ƙasar Iran bisa zargin yunƙurin shirya wani harin ta’addanci a ƙasar.
Mutumin mai shekarar 31 ana zarginsa da amfani da sinadaran makami mai guba domin shirya kai harin kamar yadda sanarwar da ‘yan sandan ta fitar ta nuna.
‘Yan sandan sun ce sun kai samame gidan mutumin wanda ke yankin Ruhr, inda suka ce sun samu sinadaran haɗa makamin mai guba.
Ofishin babban mai gabatar da ƙara na ƙara ya sanar da kama wani daban, wanda ake zargi ɗan uwa ne ga mutumin, kuma ana ci gaba da tsare mutanen biyu.
A ‘yan shekarun baya-bayan nan ƙasar Jamus na yawan fuskantar hare-haren masu iƙirarin jihadi.
Ko a shekarar 2016 ma wani hari da aka kai wata kasuwa a birnin Berlin ranar bikin Kirsimeti ya yi sanadin kashe mutum 12, tare da jikkata gommai.