Akalla ‘yan Najeriya 38 da aka kora daga Burtaniya za su isa Legas a yau a cewar, hukumomin kasar nan.
Wadanda aka koro zuwa Najeriya sun hada da iyaye da kakanni.
Wasu membobin al’ummomin LGBTQ+ da ke neman mafaka su ma suna cikin waɗanda aka kora.
Wasu daga cikin wadanda aka kora sun yi ikirarin cewa, sun zauna a Burtaniya tsawon shekaru.
Ana sa ran za su isa Legas da sanyin safiyar yau da jirgi guda daya na Home Office.
Sai dai ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta shaida wa BBC cewa, an kori mutanen ne bisa wasu laifukan da suka shafi shige da fice.