Ɗan takarar shugabancin kasa a jam’iyyar adawa ta Labour Party (LP), Peter Obi, ya roƙi ‘yan Najeriya su yi wa gwamnatin Buhari uzuri da kuma Babban Bankin Najeriya (CBN) kan sauya kuɗin ƙasar.
Ɗan takarar ya ce ba Najeriya ce kaɗai ke sauya takardun kuɗi ba kuma hakan yana da “amfani matuƙa” na tsawon lokaci.
“Ina roƙon ‘yan Najeriya su yi wa CBN da gwamnatin tarayya uzuri kuma su yi fatan al’umma da ƙasa baki ɗaya za su ci amfanin sauyin da aka yi,” kamar yadda ya bayyana cikin wasu jerin saƙonni a shafinsa na Twitter.
Sai dai ya yi kira ga CBN da kuma bankunan kasuwanci da su ƙara ƙaimi wajen yawaita sababbin takardun kuɗin ga mutane da waɗanda ba su da asusun banki “don rage wahalhalun da ‘yan uwana ‘yan ƙasa ke ciki, musamman talakawa da waɗanda ke da nisa da bankuna a ƙauyuka”.
Karanta Wannan: Peter Obi zai baku mamaki APC – Babachir Lawal
Shi ma ɗan takarar babbar jam’iyya adawa ta PDP, Atiku Abubakar, ya goyi bayan sauya kuɗin.
A gefe guda kuma, ‘yan Najeriya na ci gaba da shiga tasku wajen neman garin kuɗin da za su yi hada-hada da su, inda suke shafe awanni a kan layi kafin su samu daga bankuna.
Za a daina amfani da tsofaffin takardun N1,000 da N500 da N200 daga ranar 10 ga watan Fabarairu, kodayake CBN ya ce za a ci gaba da sauya tsofaffi da sababbi bayan wucewar wa’adin.