fidelitybank

‘Yan Najeriya za ku ci gajiyar sauya kudi na CBN – Peter Obi

Date:

Ɗan takarar shugabancin kasa a jam’iyyar adawa ta Labour Party (LP), Peter Obi, ya roƙi ‘yan Najeriya su yi wa gwamnatin Buhari uzuri da kuma Babban Bankin Najeriya (CBN) kan sauya kuɗin ƙasar.

Ɗan takarar ya ce ba Najeriya ce kaɗai ke sauya takardun kuɗi ba kuma hakan yana da “amfani matuƙa” na tsawon lokaci.

“Ina roƙon ‘yan Najeriya su yi wa CBN da gwamnatin tarayya uzuri kuma su yi fatan al’umma da ƙasa baki ɗaya za su ci amfanin sauyin da aka yi,” kamar yadda ya bayyana cikin wasu jerin saƙonni a shafinsa na Twitter.

Sai dai ya yi kira ga CBN da kuma bankunan kasuwanci da su ƙara ƙaimi wajen yawaita sababbin takardun kuɗin ga mutane da waɗanda ba su da asusun banki “don rage wahalhalun da ‘yan uwana ‘yan ƙasa ke ciki, musamman talakawa da waɗanda ke da nisa da bankuna a ƙauyuka”.

Karanta Wannan: Peter Obi zai baku mamaki APC – Babachir Lawal

Shi ma ɗan takarar babbar jam’iyya adawa ta PDP, Atiku Abubakar, ya goyi bayan sauya kuɗin.

A gefe guda kuma, ‘yan Najeriya na ci gaba da shiga tasku wajen neman garin kuɗin da za su yi hada-hada da su, inda suke shafe awanni a kan layi kafin su samu daga bankuna.

Za a daina amfani da tsofaffin takardun N1,000 da N500 da N200 daga ranar 10 ga watan Fabarairu, kodayake CBN ya ce za a ci gaba da sauya tsofaffi da sababbi bayan wucewar wa’adin.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...
X whatsapp