Mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo, ya kwatanta shugaban kasa, Muhammadu Buhari a matsayin shugaban da Ubangiji ya turo, kuma mai gaskiya .
Osibanjo ya yi wannan furucin ne yayin da ya ke horar da ‘yan Najeriya a kan su mayar da hankali wurin bunkasa baiwar da Ubangiji ya ba su, a cewarsa hakan ne babban jari.
Osibanjo a yayin da wasu wakilan Kannywood suka kai masa ziyara karkashin wata kungiyar wayar da kai mai suna 13 x 13 wadda, Dauda Rarara ya jagoranta.
Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo ya kwatanta shugaban kasa Muhammadu Buhari a matsayin shugaba mai gaskiya da Ubangiji ya turo, The Sun ta ruwaito.
Osinbajo ya shawarci ‘yan Najeriya akan mayar da hankali wurin bunkasa baiwar da Ubangiji ya ba jama’a inda ya ce, hakan babban jari ne.
Kamar yadda hadimin Osinbajo na harkar yada labaran sa, Laolu Akande ya bayyana a wata takarda, ya ce, Osinbajo ya bukaci ‘yan Najeriya su mayar da hankali akan baiwar da suke da shi don babban jari ne wanda duniya za ta gani. Osinbajo ya kira wasu daga cikin mambobin kungiyar kamar yadda The Sun ta bayyana, wadanda suka kai masa ziyara kamar Rabi’u Rikadawa da dai sauran su.