fidelitybank

‘Yan Najeriya na fama da matsanancin rayuwa – Dr Hussaini

Date:

‘Yan Najeriya har yanzu suna fama da matsin rayuwa a lokacin da suke kokarin neman abin rufin asiri, yayin da suke fuskantar tsadar kayan abinci da hauhawar farashi.

Hakan na zuwa ne wata biyar bayan gwamnatin kasar ta fitar da kuɗi har naira biliyan 72 domin shirin rage raɗaɗi, sakamakon matsin rayuwar da aka shiga bayan cire tallafin man fetur a watan Mayun bara.

Wani kwararre kan al’amuran ci gaban duniya, Dr Hussaini Abdu ya yi wa BBC bayani kan dalilin da ya sa shirin rage radadin bai cimma buri ba.

A cewar sa tallafi ba ya magani kai tsaye musamman kan abin da ya shafi tattalin arziki saboda “ana yi ne domin a cikin takaitaccen lokaci a rage nauyi, kafin ka farfado ka nemi abin yi.”

Kwararren ya ce mafi yawan al’umma sun ce an raba kayan tallafi amma ba su gani a kasa ba dalilin da ya sa ya ce ya kamata a ce an dauki lokaci ana aiwatar da tsarin tare da ware adadin da za a rika bai wa mutane.

Dr Abdu ya soki tsarin da aka bi wajen yin rabon kayan tallafin da ya ce irin tsarin ba ya “taɓa maganin talauci a ko ina.”

“Abu ne aka yi ba kan tsari ba, saboda haka ba yadda za a yi a ce ya yi maganin irin wannan abun.” in ji Dr Abdu.

Ya kara da cewa har yanzu akwai jihohin da ko “ƙwandala” ba su gani ba duk da iƙirarin gwamnati cewa ta fitar da kuɗaɗe ga jihohi domin rage raɗaɗin da al’umominsu ke fuskanta.

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp