‘Yan Najeriya har yanzu suna fama da matsin rayuwa a lokacin da suke kokarin neman abin rufin asiri, yayin da suke fuskantar tsadar kayan abinci da hauhawar farashi.
Hakan na zuwa ne wata biyar bayan gwamnatin kasar ta fitar da kuɗi har naira biliyan 72 domin shirin rage raɗaɗi, sakamakon matsin rayuwar da aka shiga bayan cire tallafin man fetur a watan Mayun bara.
Wani kwararre kan al’amuran ci gaban duniya, Dr Hussaini Abdu ya yi wa BBC bayani kan dalilin da ya sa shirin rage radadin bai cimma buri ba.
A cewar sa tallafi ba ya magani kai tsaye musamman kan abin da ya shafi tattalin arziki saboda “ana yi ne domin a cikin takaitaccen lokaci a rage nauyi, kafin ka farfado ka nemi abin yi.”
Kwararren ya ce mafi yawan al’umma sun ce an raba kayan tallafi amma ba su gani a kasa ba dalilin da ya sa ya ce ya kamata a ce an dauki lokaci ana aiwatar da tsarin tare da ware adadin da za a rika bai wa mutane.
Dr Abdu ya soki tsarin da aka bi wajen yin rabon kayan tallafin da ya ce irin tsarin ba ya “taɓa maganin talauci a ko ina.”
“Abu ne aka yi ba kan tsari ba, saboda haka ba yadda za a yi a ce ya yi maganin irin wannan abun.” in ji Dr Abdu.
Ya kara da cewa har yanzu akwai jihohin da ko “ƙwandala” ba su gani ba duk da iƙirarin gwamnati cewa ta fitar da kuɗaɗe ga jihohi domin rage raɗaɗin da al’umominsu ke fuskanta.