fidelitybank

‘Yan Najeriya mu tashi tsaye mu yi gyara – Ortom

Date:

Gwamnan jihar Benue, Samuel Ortom, ya bukaci ‘yan Najeriya da su tashi tsaye wajen ganin sun yi aiki tare domin ci gaban kasar.

Gwamna Ortom ya ba da wannan cajin ne a ranar Asabar 3 ga watan Disamba, 2022 a Fatakwal, jihar Ribas jim kadan bayan ya samu lambar yabo mafi girma a jihar, ‘Grand Serbice Star of Rivers State’ GSSRS.

Ya bayyana cewa a wannan lokaci na musamman a tarihin kasar nan da ake fuskantar kalubale a fannin tattalin arziki, zamantakewa, siyasa da tsaro, abin da kawai ake bukata shi ne jama’a su nuna kishin kasa domin ceto kasar.

Gwamnan ya yaba wa hikimar Gwamna Nyesom Wike da al’ummar Jihar Ribas da suka nuna wa Najeriya hanya ta wannan lambar yabo, wadda ta sa aka karrama jama’a a shiyyoyi shida na kasar nan.

Ya ce hakan ya nuna imanin gwamna Wike da al’ummar jihar kan hadin kan Najeriya.

A cewar Gwamna Ortom, “Idan kowane mutum a Najeriya zai yi tunani kamar Gwamna Wike, kasar za ta kasance mai girma kuma za ta dauki matsayinta a matsayin jagoran Afirka kuma babbar Afirka.”

Gwamna Ortom ya yi kira ga al’ummar kasar da cewa, a yayin da al’ummar kasar ke shirin shiga babban zaben shekara mai zuwa, kada su kalli jam’iyyun siyasa, kuma kada su kalli kabilanci, sai dai yadda za mu iya ceto kasarmu Nijeriya, mu mai da ta fiye da yadda take a yau.

Gwamnan ya yi kira ga wadanda aka karrama da su kai sakon da Gwamna da al’ummar Jihar Ribas suka isar zuwa jihohinsu da yankunansu domin jama’a su yaba da bukatar yin aiki tare domin hadin kai da ci gaban kasa.

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp