fidelitybank

‘Yan Najeriya ku yi hakuri daga ukubar da ake ji – Tinubu

Date:

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya buƙaci al’ummar ƙasa su ɗan ƙara sadaukar da kansu domin ceto ƙasar daga durƙushewa.

A cikin jawabinsa na tunawa da Ranar Dimokraɗiyya wadda ake yi duk ranar 12 ga watan Yuni, shugaba Tinubu ya ce ya san cewa matakin janye tallafin man fetur, zai haddasa ƙarin wahala ga talakan Najeriya.

Ya ce “ina jin irin raɗaɗin da kuke ji”.

Sai dai in ji shi, wannan mataki ne da dole sai an ɗauka domin ceto Najeriya daga durƙushewa da kuma ƙwato dukiyar ƙasar daga hannun wasu tsirarun mutane marasa kishi.

Tinubu ya bai wa ‘yan Najeriya tabbacin cewa haƙurinsu ba zai tafi a banza ba, bisa la’akari da yarda da kuma amanar da suka bai wa gwamnatinsa.

Shugaba Tinubu ya ce gwamnatin da yake jagoranta za ta biya ‘yan Najeriya da gagarumin ƙoƙari wajen zuba kuɗi a harkokin sufuri da bunƙasa ilmi da kuma samar da wutar lantarki, baya ga ƙoƙarin bunƙasa kula da lafiya da sauran kayan amfanin al’umma.

A cewar sabon shugaban, gwamnatinsa za ta yi hakan ne don inganta rayuwar miliyoyin ‘yan Najeriya.

Shugaban ya dai yi alƙawarin ƙara ƙwazo don cika dukkan alƙawurran da ya ɗaukarwa ‘yan ƙasar a lokacin yaƙin neman zaɓe bisa abin da ya kira manufar ‘Sabunta Fata’ wato Renewed Hope.

Tinubu ya ce tsarin dimokraɗiyyar da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa Moshood Abiola ya mutu yana gwagwarmayar tabbatarwa a Najereiya, shi ne wanda zai fifita da kuma kyautata jin daɗin al’umma a kan muradin ƙashin kai na shugabanni.

Sannan kuma da tsarin da mutanen da ake mulka za su iya cimma burin rayuwa kuma su samu farin ciki.

Bola Ahmed Tinubu a cikin jawabin nasa ya nunar cewa shekara 30 kenan cif tun lokacin da ‘yan Najeriya suka gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a 1993 don komawa ga tsarin dimokraɗiyya daga mulkin sojoji ‘yan kama-karya.

Kafin wata dokar soja ta rusa zaɓen 12 ga watan Yuni da ya bai wa Cif Moshood Kashimawo Olawale Abiola na jam’iyyar SDP nasara.

Ya ce a kowacce rana irin wannan, tsawon shekaru Najeriya za ta ci gaba da tunawa da MKO Abiola da kuma sauran gwarazan dimokraɗiyyar ƙasar kamar mai ɗakin marigayin Hajiya Kudirat Abiola wadda cikin zalunci aka yi mata kisan gilla lokacin da take gwagwarmayar tabbatar da ‘yancin talaka.

Sai kuma Pa Alfred Rewane, ɗaya daga cikin gwarazan samun ‘yancin Najeriya da kuma Manjo Janar Shehu Musa ‘Yar’adua wanda sojoji masu mulki suka rufe wa baki a lokacin da yake fafutukar tabbatar da mulkin dimokraɗiyya.

A cewar Tinubu, irin waɗannan gwaraza, sun sadaukar da “‘yancinsu ne a jiya don rayuwarmu ta yau”.

yola news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp