fidelitybank

‘Yan Najeriya ku yi hakuri da gwamnatin mai gidana – Matar Tinubu

Date:

Matar shugaban kasa Bola Tinubu, Oluremi, ta bukaci ‘yan Najeriya su yi hakuri da gwamnatin mijinta.

Uwargidan shugaban kasar ta ce gwamnatin da Tinubu ke jagoranta na aiki tukuru don ganin an bunkasa kasa da tattalin arziki.

Oluremi ta ce yana bukatar jajircewa da sadaukarwa sosai shi ne zai wadata ga ‘yan Najeriya.

Ta yi wannan roko ne a fadar shugaban kasa da ke Abuja ranar Alhamis yayin da ta karbi bakuncin Sanatocin da ke wakiltar kananan hukumomin uku na jihar Legas.

“Gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu ta kuduri aniyar barin gado ga tsararraki har yanzu ba a haife su ba. Wannan yana bukatar sadaukarwa da jajircewa,” inji ta.

Ta kuma sake nanata kiran da ta yi na ‘yan majalisar da su samar da dokar da za ta hukunta masu garkuwa da mutane a kasar.

Uwargidan shugaban kasar, wacce ta taba wakiltar Legas na tsawon shekaru 12 a majalisar dattawa, ta yi kira ga ‘yan majalisar da su jagoranci aiwatar da dokokin da suka shafi tsaro domin dakile yaduwar wannan laifi.

Tun da farko, shugaban tawagar, Sen. Adetokunbo Abiru, mai wakiltar Legas ta Gabas, ya ce sun zo ne domin yi wa uwargidan shugaban kasa gaisuwar ban girma.

Airu, Shugaban kungiyar Sanatocin Kudu, ya ce sauye-sauyen da Shugaba Tinubu ya yi na kan gaba wajen dora al’ummar kasa kan turbar tattalin arziki da ci gaba mai dorewa.

latest nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp