Matar shugaban kasa Bola Tinubu, Oluremi, ta bukaci ‘yan Najeriya su yi hakuri da gwamnatin mijinta.
Uwargidan shugaban kasar ta ce gwamnatin da Tinubu ke jagoranta na aiki tukuru don ganin an bunkasa kasa da tattalin arziki.
Oluremi ta ce yana bukatar jajircewa da sadaukarwa sosai shi ne zai wadata ga ‘yan Najeriya.
Ta yi wannan roko ne a fadar shugaban kasa da ke Abuja ranar Alhamis yayin da ta karbi bakuncin Sanatocin da ke wakiltar kananan hukumomin uku na jihar Legas.
“Gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu ta kuduri aniyar barin gado ga tsararraki har yanzu ba a haife su ba. Wannan yana bukatar sadaukarwa da jajircewa,” inji ta.
Ta kuma sake nanata kiran da ta yi na ‘yan majalisar da su samar da dokar da za ta hukunta masu garkuwa da mutane a kasar.
Uwargidan shugaban kasar, wacce ta taba wakiltar Legas na tsawon shekaru 12 a majalisar dattawa, ta yi kira ga ‘yan majalisar da su jagoranci aiwatar da dokokin da suka shafi tsaro domin dakile yaduwar wannan laifi.
Tun da farko, shugaban tawagar, Sen. Adetokunbo Abiru, mai wakiltar Legas ta Gabas, ya ce sun zo ne domin yi wa uwargidan shugaban kasa gaisuwar ban girma.
Airu, Shugaban kungiyar Sanatocin Kudu, ya ce sauye-sauyen da Shugaba Tinubu ya yi na kan gaba wajen dora al’ummar kasa kan turbar tattalin arziki da ci gaba mai dorewa.